An maka yan Najeriya hamsin a bangarori daban-daban da suka hada da mawaki David Adeleke, jagorar #BringBackourGirls, Aisha Yesufu da kuma Fasto Sam Adeyemi a gaban kotun majistare da ke Abuja.
An kai su kotu ne a kan rawar ganin da suka taka a zanga zangar EndSARS da aka yi kwanan nan. A karar da wani mai fafutukar kare hakkin dan adam, Kenechukwu Okeke ya shigar, ya zargi wadanda ake karar da amfani da shafin Twitter wajen haifar da hargitsi da sunan zanga zangar EndSARS wanda daga bisani ya zama rikici
Okeke ya ce aikin wadanda ake karar laifi ne da hukuncinsa yake a karkashin sashi na 97(2) na Penal Code Act, C53 dokar tarayyar Najeriya, 2004. Ya wallafa a shafin Twitter: “Bayan shigar da kara a kan wadanda suka bunkasa rikicin #EndSARS da karfe 1052hrs WAT, 09/11/2020, za mu tannatar da ganin cewa an hukuntasu saboda tsaro, da kuma kariyar jama’a.” Tarayyar Najeriya kasa ce mai dokoki.
Aisha Yesufu
Oseni Etomi
Yemi Eberech Alade
David "Davido" Adeleke
Damini "burnaboy" Ogulu
Kanu Nwankwo
Kiki Mordi
Peter Okoye
Paul Okoye
Deji Adeyanju
Tiwa Savage
Feyikemi Abudu
Debo Adebayo
Folarin "Falz" Falana
Maryam "Taoma" Akpaokagi
Dr. Joe Aba
Bankole Wellington
Uche Jombo
Rodriguez Ayo "AY"
Makun Japhet
Omojuwa Ikuforiji
AbdulRahmon Jola
Ayeye Laila
Johnson-Salami
Anita "Tacha" Natacha
Akide Temitope
Majekodunmi Fakhriyyah Hasim
Oghenekaro Ibada Omu
Chbuzor Nelson
Ayo Sogunro
Pamilerin Adegoke
Chinedu Okoli
Micheal Collins
Ajereh (Don Jazzy)
Yul Edochie
Ojabodu Ademola
Oduola Rinu
Tope Akinyode
Ogbeni Dipo
Small Doctor Flavour
Agbelese Olamilekan
Layo Ogunbanwo
Kelvin Shekahu Runtown
Ibrahim Wizkid Balogun
Damilola Odufuwa
A gefe daya, Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya yi gargadin cewa Najeriya na iya fuskantar sabuwar zanga zanga idan gwamnati ta gaza magance rashin aikin yi na matasa.
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari