Wamakko ya dauki nauyin karatun matasa 45 a Jami’ar Ibadan


Tsohon Gwamnan Sakkwato, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko, ya dauki nauyin karatun matasa 45 ‘yan asalin jihar Sakkwato a Jami’ar Lead city da ke birnin Ibadan na jihar Oyo domin karatun digiri na daya.

Sanata Wamakko a lokacin da yake bai wa daliban takardun gurabun karatun da suka samu, ya roke su da su mayar da hankali a wurin karatunsu.

Tsohon Gwamnan ya shawarci matasan a kan kada su yi wani abu da zai kawo wa karatun cikas, kuma kada su yi wasa da wannan damar da Allah ya basu ta sanadiyarsa.

Ya kuma yi kira gare su a kan kada su yi duk wani abu da zai kawar da martabar danginsu da jihar Sakkwato, yana cewa “ilmi shi ne abu mafi kima da za ka bai wa mutum a rayuwa.”

“Makudan kudin da aka kashe na ganin kun samu wannan damar kar ku yi wasa da ita ku zama jakadu nagari.”

“Ku tabbata ba ku shiga cikin kungiyoyi irin na asiri da wasu za su bata tarbiyarku ba, don gudun da na sani a cikin rayuwa” inji Wamakko.

Matasan za su karanci kwasa-kwasan Injiniyanci da Likitanci domin kara bunkasa fannin ilmi a jihar Sakkwato.

Bayan daliban da za su karanci Injiniyanci da Likitanci akwai masu karatun sanin makamar aikin gwamnati da Sadarwa da Kimiya da sanin halayyar dan Adam da sauransu.

Source: Jaridar Aminiya


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN