Saurayi da ya kashe yar shekara 8 bayan ya karbi kudin fansa N500,000 ya shiga hannu a Kano


Rundunar yansandan jihar Kano ta kama wani saurayi dan shekara 24 mai suna Habibu Sale bisa zargin kashe wata yarinya yar shekara 8 bayan ya saceta ya yi garkuwa da ita kuma ya karbi kudin fansa har  N500,000 daga iyayenta.

Kakakin hukumar yansandan jihar Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar cewa  yansanda sun kama wanda ake zargin ranar Talata 17 ga watan Nuwamba. Ya ce Sale ya sace yarinyar mai suna Asiya Tasiu a kauyen Chikawa, da ke karamar hukumar Gabasawa ranar 6 ga watan Yuni 2020, lokacin da aka aiketa gidan Antinta da ke makwabtaka da gidansu.

An samo cewa ya bukaci a bashi N10m da farko, amma bayan tattaunawa ta fahimta, an ba shi N500,000.

DSP Haruna ya ce yan sanda sun yi nassarar kama  Sale ranar 7 ga watann Nuwamba bayan sun bi diddiginsa daga jihohin Jigawa, Katsina, Kaduna, Abia  da Kano inda aka cafke shi yayin da yake zaune a kofar gidansu.

Binciken yansanda ya nuna cewa Habibu ya kashe yarinyar ne saboda ya san za ta gane shi, kuma za ta tona masa asiri idan ya sake ta, saboda suna makwabtaka. Sakamakon haka ya kashe ta ya bizine gawarta a gefen kauyen Chikawa.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN