Hukumar Hisbah na jihar Kano ta kone kwalabe Miliyan daya da dubu dari tara da saba'in da biyar (1,975,000) na kimanin kudi Naira Miliyan dari biyu. N200m.
An gudanar da kone kwalaben giyar ne ranar Lahadi 8 ga watan Nuwamba a Kalebawa da ke karamar hukumar Dawakin Tofa karkashin jagorancin Gwamna Umar Ganduje.
Yayin da yake jawabi a wajen kone kwalaben, Gwamna Ganduje, wanada mataimakinsa Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya wakilta ya ce, shan barasa tare da wasu ababen da ke sa maye kuma ke gusar da hankalin dan Adam, Musulunci ya haramta mu'amala da su.
Rahotun Isyaku Garba
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari