An ceto mutum 11 daga hannun masu sace mutane domin karban kudin fansa a jihar Zamfara tare da taimakon Gwamnan jihar Zamfara.
Rahotanni sun ce Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle ne ya yi sanadin kubutar mutanen kuma ba tare da biyan kudin fansa ba.
Sakataren watsa labarai na Gwamnatin jihar Zamfara Jamilu Iliyasu Magaji ne ya sanar da haka ranar Lahadi da dare.
Ya ce wannan ya samu ne sakamakon wani shirin Gwamnati na "Karas ko icce". Ya ce Gwamnati za ta yi duk abin da za ta iya yi domin bayar da tsaro ga al'umman jihar Zamfara.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari