Fusatattun matasa sun yi wa wasu da ake zargin yan yan fashi da makami ne mugun duka har suka mutu, daga bisani aka banka wa gawarsu wuta a garin Benin na jihar Edo.
Lamarin ya faru da sanyin safiyar ranar Talata 3 ga watan Nuwamba, kusa da kasuwar Okah da ke hanyar Ighodefeyi a kan hanyar Sokponba.
An zargi matasan guda biyu da yi wa mata masu zuwa kasuwa da sassafe fashi, tare da jama'a da ke zuwa wajen aiki.
Fusatattun matasa sun yi amfani da duk makami da za su iya amfani da shi wajen afka wa yan fashin.
Bayanai sun ce bayan tarzomar EndSars da ya yi sanadin kone ofisoshin yansanda guda uku da ke . St Saviour, Ugbegun da Idogb. Yanzu haka babu jami'an tsaro a wannan yankin, lamari da ya sa bata gari ke ta cin karensu ba babbaka.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari