An tsinci gawar wata budurwa wacce ke aikin nishadantarwa mai suna Ijeoma Neke an yabe jikinta da sinadarin Asid yashe a gefen titi kwanaki kadan bayan bacewarta.
Ijeoma ta bar gida tun ranar Laraba 11 ga watan Nuwamba domin ta je wajen aiki, sai dai tun wannan ranar bata dawo gida ba.
ISYAKU.COM ya samo cewa, bayanai sun ce ta bukaci ta san inda za ta je ta yi aiki, amma wanda ya gayyace ta ya ce ta je wajen tsayawar mota da ya gaya mata daga nan ba a sake ganinta ba.
Daga bisani an ga gawarta a unguwan Maryland da ke birnin Enugu kuma a jike ta da sinadarin Asid kamar yadda wasu masu tausayawa suka yi zargi a shafukan yanar gizo.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari