Labarin dake shigo mana da duminsa na nuna cewa wasu matasa sun kai hari gidan gyaran halin jihar Ondo kuma sun saki fursunonin dake ciki.
Bidiyon da wani Fasanmi Paul ya daura shafins ana Facebook ya nuna yadda fursunonin ke kokarin fitowa.
A cewar rahoton Channels TV, akalla fursunoni 58 sun gudu daga gidan gyara halin kuma sun bankawa gidan yarin wuta dake karamar hukumar Ikitipupa na jihar.
A cewar rahoton, kakakin hukumar yan sandan Ondo, ASP Tee Leo-Ikoro ya tabbatar da hakan a hirar wayar tarho.
A cewar masu idanun shaida, wasu jami'an tsaro sun samu rauni amma babu tabbaci ko an rasa wani tukun.
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari