Ministan jinkai da bayar da agajin gaggawa Sadiya Umar-Farouq ta ce ma'aikatarta ta bayar da taimakon Naira biliyan N6b ga talakawa a kananan hukumomi 14 na jihar Zamfara. Ta yi wannan jawabi ne ranar Talata 27 ga watan Oktoba a jihar Zamfara.
Ta ce an tura wa talakawan kudaden ne karkashin shiri na musamman na tura kudi da ake kira 2020 Conditional Cash Transfer (CCT).
Ta ce talakawa 130,000 ne suka amfana da shirin daga kananan hukumomin Anka, Bungudu, Birnin Magaji, Kaura Namoda, Tsafe, da Talata Mafara.
Ta ce wadanda suka amfana sun sami daga N30,000 zuwa N80,000 wanda ya danganta da lokacin da suka cika takardun neman taimakon.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari