An kama dansanda da ya harbi budurwarsa da bindiga a baki kuma ya gudu


An kama wani dansanda bayan ya harbi budurwarsa da bindiga a baki kuma ya tsare ranar 8 ga watan Satumba a birnin Lagos.

ISYAKU.COM ya samo cewa dansandan ya harbi dudurwarsa mai suna Joy Eze da bindiga ne lokacin da suke zazzafar cacan baki tare da ita, sai ya sa bindiga ya harbe ta a baki, daga bisani ya gudu. Bakin Joy ya yage sakamakon harbin, kuma aka garzaya zuwa Asabiti da ita.

Kakakin yansanda jihar Lagos Muyiwa Adejobi ya sanar da haka a sanarwa da ya fitar, ya ce an kama SGT Eze Aiwansone na sashen yansandan tsaron lafiya SPU Base 16 da ke Ikeja.

Adejobi ya ce SGT Eze ya gudu bayan ya aikata barnar, amma wani yayansa ne ya kamo shi ya kawo shi gaban yansanda domin shi ma Safeton yansanda ne.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN