Wasu rahotanni dake futowa daga ologbo karamar hukumar Ikpoba Okah, Jihar Edo sun bayyana cewa an harbe wani mutum, wanda yanzu haka ba a bayyana halin da yake ciki ba.
Da aka tuntube shi kan zargin harbe-harben a Ologbo Dukedoom, Enogie, HRH Jason Owen Akenzua, ya ce ya ji karar harbe-harbe kuma lokacin da ya tuntubi DPO, sai aka gaya masa cewa ’yan sanda ne suka yi harbi a lokacin da wurin ya hartsu ne.
“Na ji karar harbe-harbe sai na kira DPO Ologbo. Ya ce ‘yan sanda ne suka yi harbe-harben don gargadi lokacin da wurin ya hautsine ya rikice. Amma yanzun Yankin ya samu kwanciyar hankali da lumana. ”
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/