‘Yan ta’adda sun kwacewa ‘yansandan Najeriya Bindiga sun kashe mtum 1


Rahotanni daga jihar Imo sun bayyana cewa, ‘yan ta’adda a Egbu dake Owerri da Owerre Nkworji dake karamar hukumar Nkwerre sun kaiwa ‘yansanda hari inda suka kwace musu bindigu da kuma daddatsa daya daga ciki wanda hakan yayi sanadiyyar mutuwarsa.


Ranar Litinin ne ‘yan Bindigar suka kaiwa ‘yansandan dake Nkwerre hari inda suka daddatsa daya daga ciki sannan suka kona motar aikin ta ‘yansandan.

 

An garzaya da wanda aka sara Asibiti ranar Talata saidai daga baya ya rasu, kamar yanda Rahoton Punch ya tabbatar.

 

Hakanan kuma wasu ‘yan Bindigar sun kai wa ‘yansanda hari a Egbu inda suma suka kwace musu bindigu da sarar wani dansanda amma daga baya an garzaya dashi Asibiti.

 

Kwamishinan ‘yansandan Jihar, Isaac Akinmoyede da aka tuntubeshi ya tabbatar da cewa, an kwacewa ‘yansandan Bindigu amma babu wanda aka kashe

Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN