Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, ta zartar da dokar yi wa masu fyade dandaka.
Majalisar ta sanar da kammala zartar da dokar mai lakabin “Kaduna State Penal Court Law No.5 of 2017” a turance.
A bisa wannan hukuncin doka, daga yanzu duk wanda aka kama da laifin fyade kuma aka tabbatar da ya aikita hakan, to ko shakka babu, za a yi masa dandaka.
Idan dai ba’a manta ba, a cikin watan da ya gabata ne, Matar Gwamnan Jihar kaduna, Hajiya Aisha Ummi Garba Elrufai, ta kai rokon ta gaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, a kan su taimaka su yi gyaran dokar domin a yi hukunci mai tsanani a kan duk wani da aka kama da laifin aikata fyade a fadin Jihar.
Source: Leadership Ayau
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/