Rahotanni sun ce wani mai sana'ar Acaba ya ketare rijiya da baya bayan wasu da suka dauke shi haya sun yi masa datsan kubewa da adda ranar 29 ga watan Satumba.
Bayanai sun ce mai Acaban ya dauki mutanen ne wadanda suke sanye da kakin soji, daga mahadar Leru da ke Umuchieze kuma suka bukaci ya ajiye su a Nneato a jihar Abia.
Sai dai an yi zargin cewa bayan sun isa kusa da Jami'an Spiritan da ke Nneochi, sai suka tilasta shi ya shiga daji da su . Daga bisani suka daure shi kuma suka daddatsa shi da adda, suka gudiu da babur da ya dauko su da shi.
Dan Acaba dai ya farfado daga baya, ya sami damar kwance kanshi, kuma ya lallaba ya yi rarrafe zuwa kusa da bakin titi, inda wasu mutane suka taimakke shi.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/