Gidaje 150 sun rushe a garin Tureta sakamakon cushewar Dam


Mazauna garin Lambar Tureta mai nisan kilomita kimanin hamsin kan hanyar da ta hada jihohin Sakwkwato da Kebbi da kuma sauran jihohin arewacin Nijeriya suna fuskantar barazana daga wata karamar madatsar ruwa da ke wajen garin sanadiyyar cushewa da ta yi wanda hakan ya sanya akalla sama da magidanta dari da hamsin kaura zuwa cikin garin Tureta  wadansu kuma su ka canza unguwa.

Mukaddashin Shugaban Karamar hukumar mulki ta Tureta Honarabul Hassan Muhammad Tureta ya bayyana haka a jiya Laraba yayinda ya ke zantawa da wakilinmu a garin Tureta.


Honarabul Hassan ya ce wannan karamar madatsar ruwan saboda sanin muhimmancin ta gun jama’a ya sanya tun shekaru uku da suka wuce an sha kai koken Cushewar ta ga gwamnatin jihar Sakwkwato amma dai ba a ci nasara ba  Yanzu haka da zarar aka yi ruwan sama maimakon ruwan ya taru a wannan madatsar ruwan sai ya shigo gidajen mutane wanda a sanadiyyar haka ba Wai gidaje kadai ba har wannan babbar hanyar da ta hada jihohin arewacin Nijeriya da kuma Sakwkwato tana neman halaka sabodada zarar an soma ruwan sama duk uzurin da mutane ke da shi sai dai su hakura har sai bayan wani lokaci mai tsawo idan an dauke ruwan.

\
Ya kara da cewa ba matsalar madatsar ruwan sama kadai ke barazana ga jama’ar karamar hukumar mulki ta Tureta ba har ma da ruwan sama da ya ke akwai fadamu sosai zagayen karamar hukumar kuma babu inda ruwan bai yi barna ba duk da ya ke babu wata sahihiyar kididdiga amma a jimlace sama da magidanta dubu biyu ne suka rasa gidaje da kuma amfanin gona.


Bayan Jajantawa ga al’ummar da abin ya shafa ya kuma yi kira ga hukumomin da ke da hakki da su kawo  agaji duk da ya ke har yanzu dai ba a sami labarin salwantar rayuwa ba sai dukiya mai yawa.
Yayin da wadansu ke neman mafaka a sanadiyyar ambaliya  a daya bangaren kuma wadansu kariya su ke baiwa muhallansu inda garin Makera da ke yammacin babban Birnin jihar Kebbi ruwa ne ya dauko sabuwar hanya ya nufo garin inda su kuma al’ummar garin musamman matasa sun fito kwansu da kwarkwata don baiwa gidajensu kariya duk da ya ke dai ruwan har ya soma canye wadansu gidaje da ke kusa da rafi.


Malam Usman wani matashi ya bayyana cewa ba su taba ganin irin wannan tashin hankali ba saboda ruwan ba abinda ke iya tariyarsa saboda tafiyar da ya ke da karfin gaske, mu na dai iya kokarin mu ne muga ruwan In Sha Allahu bai yi barna mai yawa ba.


Ya ce dan majalisa zartaswa mai wakiltar karamar hukumar mulki ta Birnin Kebbi Honarabul Hassan Namaroko bai yi kasa a gwiwa ba da jin halinda su ke ciki ya zo ya ga irin yadda wajen ya ke sannan kuma ya yi alkawarin isar da korafin inda ya dace tun kama daga matakin jiha zuwa na tarayya.


Yanzu haka dai a jihar Kebbi kusan duk kananan hukumomin da ke kusa da fadamu ba wacce ba a sami barazana daga ambaliya ba wacce ta tilastawa wadansu magidanta hijira yayinda su kuma  hukumomin da abin ya shafa da wakilai da shugabanni sai kai komo su ke yi ba dare ba rana don ganin mutane sun sami matsugunansu kafin damina ta wuce.

Source: Leadership Ayau


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN