Malamin Islamiyya ya yi wa yar shekar 15 fyade da sunan zai taimaketa ta cire cikin shege

Rundunar yansandan jihar Ogun ta kama wani Malamin Islamiyya dan shekara 38 mai suna Ismaila Saheed da Toliha Sabith mai shekara 20 bisa zargin yi wa karamar yarinya mai shekara fyade 15.

Rahotun yansanda ya ce Sabith ne ya fara yi wa yarinyar fyade a unguwar Imedu-nla da ke garin Mowe. Daga bisani yarinyar ta kai kara wajen Malamin Islamiyya wanda shi kuma ya yi amfani da wannan dama ya yi mata fyade da sunan zai taimaketa domin a cire cikin gaba da fatiha da ta dauka bayan saduwar farko da Sabith.

Bayan yarinyar ta shigar da kara wajen yansanda, DPO Bala Yakubu, ya umarci yansanda masu bincike su kamo Malamin tare da Sabith, wanda suka amsa laifinsu yayin binciken yansanda. An mika mutanen zuwa sashen bincike na SCIID domin fadada bincike kan lamarin.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN