Yansanda sun kama Namalika wanda ake zargin ya kashe Likita a Zamfara ya kone gawarsa

Yansandan jihar Zamfara sun kama wani mai suna Abubakar Namalika bisa zargin kashe wani Likita mai suna Dr. Enoch Okpara a Gusau.

Ranar 13 ga watan Yuni ne aka tarar an kashe tare da kona gawar wannan Likita a gidansa da ke unguwar Mareri a birnin Gusau.

Kwamishinan yansandan jihar Zamfara Usman Nagogo ya shaida wa manema labarai haka.

Ya ce yansanda sun kama Namalika ne yayin da suke kokarin aikata wani laifin, amma sauran yan gungun nashi sun gudu.

Ya ce Namalika ya shaida wa yansanda cewa su ne suka aikata laifin, sun je gidan Likitan ne domin su karbi kudi ko ta halin dole, bayan basu sami kudi a wajensa ba sai suka kashe shi suka kone gawarsa.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN