Al'ummar
garin Zakka a jihar Katsina sun ce wasu 'yan bindiga da ba su san ko su
waye ba sun kai masu hari inda suka sace mata 17 da kuma kwashe shanu
da dukiyoyinsu.
Wani
mazauni garin na Zakka da ke cikin ƙaramar hukumar Safana ya shaida wa
BBC cewa Æ´an bindigar sun shiga garin ne tsakar daren Lahadi inda suka
shafe sama da sa'a biyu suna fashi.
Ya
ce Æ´an bindigar sun shigo garin ne misalin karfe 12 na dare kuma suka
fara harbin bindiga wanda ya razana mutanen garin wasu suka ruga daji
wasu kuma suka boye a cikin karan dawa da gero.
"Sun
kwashe shanu da dama da tumaki sannan suka shiga gida gida suna kwatar
dukiyar mutane kafin su tafi da mata da 'yan mata 17," inji shi.
Amma
ya ce É“arayin sun mayar da wata yarinya Æ´ar wata biyar da haihuwa da
kuma hudu daga cikin matan da suka ɗauka da ya ce suma Allah ya kuɓutar
da su.
Ƴan bindigar dai ba su kashe kowa ba a garin na Zakka wanda a bara aka taba kai wa hari.
Babu dai wani bayani da ya fito daga jami'an tsaro game da harin.
Jihar
Katsina na É—aya daga cikin jihohin da 'yan bindiga ke ci gaba da cin
karensu babu babbaka a yankin arewa maso yammacin Najeriya.
Rahotanni
daga wasu ƙauyuka na jihar irin su Batsari da Dutsinma da Jibiya da
Faskari na cewa kaso mai yawa na manoman yankin ba su yi sharar gona ba a
wannan shekara ballantana niyyar fara noma sakamakon matsi da suke
fuskanta daga 'yan bindiga.
Source: BBC
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/