Rahotun hutudole
Gwamnatin tarayya ta sanar da Sharuddan bude makarantu a yau Litinin, duk da dai bata sanar da ranar bude makarantun ba.
A sanarwar da Ma’aikatar Ilimi ta fitar wadda ke da sa hannun Ministan Ilimi, Adamu Adamu da kuma karamin Ministan Ilimi, Chukwuemeka Nwajuiba tace akwai bukatar samar da abubuwan wanke hannu.
Sanarwar tace, an samar da ka’idojin bude makarantunne bisa hadin gwiwar Ma’aikatar Lafiya da kuma ta Muhalli da wasu masana kiwon Lafiya a kasarnan.
Sanarwar tace dolene a yi kokarin ganin an bada tazara wajan zaman dalibai a ajujuwa sannan ta kuma bayyana aniyar samar da jarin ajujuwa da sauran kayan da ake bukata dan tabbatar da wadannan dokoki sun yi aiki.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari