Allah gatan talaka: Almajirai 193 sun kamu da cutar Korona a jihar Kano - Inji Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano ta sanar cewa Almajirai 193 sun kamu da cutar Korona a jihar.

Kwamishinan Ilimi na jihar Sanusi Muhammad Kiru ya sanar wa Manema labarai haka ranar Alhamis a lokacikin wani taro da  manema labarai.

Ya ce an killace akalla mutum 1860 a Cibiyoyi guda uku da aka tanada don killace masu cutar a fadin jihar,  wanda aka sami mutum 193 dauke da cutar a cikin adadin mutanen da aka killace.

Sanusi, wanda shi ne babban jami'in Gwamnatin jihar Kano da ke kula da lamarin Almajirai a jihar, ya ce Almajirai 86 sun kamu da cutar a gwajin da aka yi a wajen killacewa na Gabasawa, 68 a wajen killacewa na Karaye sai kuma 38 a Kiru.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN