An kama wanda yawa ‘yar shekaru 14 fyade ta dauki ciki kuma ya yadda jaririn a Sokoto

Jami’an ‘yansanda sun kama wani Sha’aibu Aliyu a garin Kalambaina dake karamar Hukumar Wammako dake jihar Sakkwato da zargin yiwa wata yarinya da ba’a  bayyana sunan ta ba me shekaru 14 fyade wanda kuma har ta haihu.

Bayan haihuwartane sai ta kai masa jaririyar amma sai shi da wani abokinsa, Nasiru Attahiru suka je suka jefar da ita a jeji.

Saidai Allah ya taimaka wasu suka ga Jaririyar suka kaiwa mahukuntan karamar hukumar Wammako wanda su kuma suka kaiwa ‘yansanda kara.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Sani Kaoje ya tabbatar da faruwar lamarin inda suka ce abokin Shu’aibu da suka yi aika-aikar tare ya tsere amma suna kan nemanshi.

Yace akwai kuma wani mutum shima, Ahmad Alhaji Dahiru Maibuhu da yawa wata yarinya me shekaru 12 fyade wanda an kamashi. Lamarin ya farune a Rumbukawa dake Illela.

Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN