Yan fashi sun kashe wata daliba bayan sun yi mata fyade

An kashe wata dalibar kwaleji da aka sassara da adda bayan an yi mata fyade a cikin coci.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Oyo ta ce Grace Oshiagwu ta rasu ne bayan matsfan sun yi mata fyade sun kuma sassare ta.

Aminiya ta ruwaito cewa aika-aikan na zuwa ne kimanin makonni biyu da aka yi wa wata budurwa mai suna Barakat Bello fyade aka aka kuma kashe ta a yankin.

A karamar Hukumar ta Akinyele ce kuma aka yi wa wata mata mai juna biyu da ke karatu a jami’a fyade aka kuma kashe ta.

Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Oyo Olugbenga Fadeyi, ya kara da cewa, “Mun fara gudanar da bincike da kokarin gano miyagun domin a hukunta su.

“Muna rokon duk mai wani kwakkaran bayani da ya taimaka domin mu magance wannan danyen aiki”, inji shi

Rahotun Aminiya

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN