Yadda matar marigayi tsohon gwamnan Oyo ke caccakar mataimakin gwamna, Ganduje na bata hakuri

A yayin da tawagar wasu gwamnoni suka jewa iyalan marigayi Tsohon gwamnan jihar Oyo, Sanata Abiola Ajimobi ta’aziyyar rashinshi da aka yi an samu wata ‘yar Dirama.

Matar marigayin,  Madam Florence ta caccaki mataimakin gwamnan jihar, Mr. Rauf Olaniyan inda ta bayyana cewa mutum dai mai tsoron Allah ya kamata idan an yi rasuwa irin wannan ko a wayane ya kira yayi gaisuwa

Tace ko kai ma ya kamata ace ka kira a waya ka maja ta’aziyya. Saidai yace mata ya kira ba’a sauka ba.

Ta mayar masa da cewa me yasa bai aiko da sako ba tunda bata da lambar wayarsa, kuma ita matar dan siyasa ce ba zata rika daukar lambobin wayar da bata sani ba.

A karshe dai tace mijinta ya bautawa jihar kuma ya mutu, kuma kowa ma zai mutu.Gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje dake wajan da sauran gwamnoni sun saka baki inda suka baiwa duka bangarorin biyu baki akan a yi hakuri.

Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN