Tsawa ta fada kan ofishin FRSC a jihar Kudu ta kashe jami'ai 3 ta buga fiye da 12 a kasa

Tsawa ta fada wa ofishin jami'an FRSC na Itele-Ijebu da ke kan hanyar Ijebu-Ode-Ore ta kuma kashe mutum uku ta watsar da sauran mutane a kasa ranar Laraba 17 ga watan Yuni da sanyin safiya.

Lamarin ya faru da misalin karfe 10 na aafe a tsohon Toll gate na tagwayen hanya, wanda haka ya jefa rundunar jamai'an FRSC na jihar Ogun cikin alhini.

Mun samo cewa jami'an suna kokarin gudanar da paretin safe da aka saba a harabar ofishinsu, sai tsawa ta fada masu. Nan take mutum 3 suka mutu , saura kuma suka fadi sakamakon radadin wutan lantarki da tsawar ta watsa masu wanda ya shafi fiye da mutum 12.

Jami'in wayar da kan al'umma da fadakarwa na rundunar FRSCna jihar Ogun Florence Okpe ya tabbatar da faruwar lamarin, sai dai ya ki ya ce uffan ko karin bayani.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN