Mai ba shugaban kasa shawara kan harkar tsaro Babagana Munguno NSA, Safeto Janar na yansandan Najeriya IGP Muhommed Adamu, DGSS Yusuf Magaji, sun ziyarci jihar Katsina ranar Laraba 17 ga watan Yuni bayan wani zanga zanga da matasa suka yi kan tabarbarewar tsaro a jihar.
Idan baku manta ba, yan bindiga sun yi ta kai hare haren rashin imani kan bayin Allah a fadin jihar, lamari da ya zama babban kalubale da jihar Katsina ke fuskanta a halin yanzu.
A lokacin ziyararsu, tawagar ta zarce zuwa gidan Gwamnatin jihar Katsina kuma ta gana da Gwamna Aminu Masari tare da wasu muhimman mutane kan harkar tsaro har na tsawon awa biyu.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI