Type Here to Get Search Results !

Kashe DPO da yansanda 7 a jihar Kogi, duba matakin gaggawa da IGP ya dauka kan yan fashi

Yansanda 8 tare da farar hula 1 sun mutu a garin Isunlu a jihar Kogi ranar Alhamis bayan wasu miyagun yan fashi da makami sun farmaki garin.

DPO na yansanda na cikin yansanda da yan fashin suka halaka bayan sun kai hari a ofishin yansandan, suka saki wadanda aka tsare, daga bisani suka harbe yansandan har lahira.

Rahotanni sun ce bayan yan fashin sun halaka yansandan, sai suka zarce zuwa wani Banki suka kwashi kudi da ba a san adadinsu ba.

Sakamakon haka shugaban yansandan Najeriya Muhammed Adamu ya bayar da umarnin kaddamar da gagarumin bincike domin kama yan fashin da suka yi wannan aika aika.

Hukumar yansandan Najeriya ta fitar da wannan sanarwa a shafinta na Twitter, cewa shugaban yansanda Muhammed Adamu ya abayar da umarnin yin binciken kwakwaf kan lamarin.

Tuni Shalkwatan yansandan Najeriya ta aika kwararrun jami'anta na sashen Intelligence Response Team (IRT), da Special Tactical Squad (STS) da Federal-SARS suna cikin wadanda IGP ya tura jihar Kogi domin su binciko, kuma su kamo wadanda suka aikata wannan danyen aiki ga jami'an yansanda.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.
Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN