Hotuna: An kashe dalibar Jami'a mai dauke da juna biyu tsawon wata 7

An sami gawar wata daliba wacce ke karatu mataki na Digiri na biyu mai suna Shomuyiwa Azeeza wacce ke dauke da juna biyu tsawon wata 7 a dakinta a Jami'ar jihar Oyo da ke birnin Ibadan.

Bayanai sun ce an ga alamar cewa an yi amfani da katon dutse ne aka doke ta a kai.

Sai dai wata sanarwa da hukumar Jami'ar ta fitar ya musanta cewa an yi wa dalibar fyade ne har ta mutu kamar yadda labari ya watsu a shafukan sada zumunta.

Hakazalika bayanai sun tabbatar cewa Kwamishinan yansandan jihar Oyo ya je har dakin dalibar kuma tuni yansanda suka fara gudanar da bincike kan musabbabin dalibar.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN