An kama mutane 40 da laifin yi wa yara fyade da luwadi a jihar Katsina

R
undunar ‘yan sanda ta jihar Katsina, karkashin jagorancin kwamishinan Yan Sanda Alhaji Sanusi Buba ta yi nasarar cafke wadanda ake zargi da yi wa kananan Yara fyade da kuma luwadi har su sama da arba’in daga watan Aprilu zuwa watan Yuni na wannan shekarar da muke ciki.

Kwamishinan ‘yan sanda, Sanusi Buba, wanda ya samu wakilcin Kakakin rundunar ‘yan sanda SP Gambo Isa, a lokacin da yake baje kolin masu laifin a helkwatar rundunar da ke Katsina.Wadanda aka kamo masu aikata wannan muzgunawa kananan Yara maza da mata, an kamo su daga kananan hukumomi talatin da hudu na jihar Katsina.

Kuma akwai masu mabanbanta shekaru ne. Akwai masu shekaru sittin da biyar har zuwa ashirin. Akwai wanda ya yiwa kanwarsa fyade wanda suke uba daya. Akwai kuma wadanda suke da wani rukuni, wanda kowa sai ya yi lalata da wadanda suka samu.

Akwai wani Mai waka yabo, da ake zargi da dauko wani yaro daga garin su Abukur, ya kawo shi cikin garin Katsina, yana lalata da shi ta Dubuta. Akwai dan shekara ashirin da ya yiwa yar shekara biyar fyade.

Duk a cikin su akwai dan shekara sittin da biyar da ya lalata kananan yara guda ukku. Mafi yawancinsu sun amsa laifukkan su.Kwamishinan ya ce da zaran an kammala bincike za a maka su gaban kuliya manta sabo, wasu kuma tuni an fara gurfanar da su gaban kotu. Kuma ya yi kira ga iyaye su dunga kula da suwa yayansu ke mu’amala ta yau da kullum.

Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN