Da Dumi-Dumi: Liverpool ta lashe kofin Premier League

K
ungiyar kwallon kafa ta Liverpool ta lashe kofin Premier League a daren yau bayan Chelsea tawa Manchester City 2-1 a wasan da suka buga a daren yau.Christian Pulisic ne ya fara ciwa Chelsea kwallo inda Kevin De Bruyne ya farketa.

Willian ya ciwa Chelsea kwallon daga kai sai gola bayan da Fernandinho ya taba kwallo da hannu wadda tasa aka bashi jan kati.Shekaru 30 kenan Rabon Liverpool da Kofin wanda a wannan shekarar ta lashe bayan ta yi nasara a wasanni 28 cikin 30 data buga.

Har yanzu akwai sauran wasanni 7 da zata buga wanda hakan yasa ta kafa tarihin da babu kungiyar data taba kafashi, a baya dai Manchester United da City sun lashe kofin Premier League da sauran wasanni 5 da za’a buga.

Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN