Za a rataye matashin da ya kashe mahaifiyarsa da kannensa biyu a Gusau

Rahotun JaridarAminiya

Wata babbar kotu da ke Gusau  babban birnin jihar Zamfara ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya akan wani matashi mai suna Kamal Yusuf bayan samun shi da laifin kashe mahaifiyarsa da kuma kannensa mata guda biyu.

Gwamnatin jihar Zamfara ce dai ta gurfanar da matashin a gaban kotun jihar tare da wasu mutum biyu da suka hada da: Armaya’u Shehu da kuma Caleb Humphrey akan aikata laifuffuka guda uku.
To sai dai daya daga cikin wadanda ake tuhuma din mai suna Caleb Humphrey ya mutu yayin da ake sauraren shari’ar.

Laifukan dai sun hada da: hada baki domin aikata laifin fashi da makami da kuma aikata kisan kai wanda kuma hukuncinsa kisa ne matukar an samu wanda ake zargi ko tuhuma da aikata hakan.
Da take yanke hukuncin, babbar jojin jihar ta Zamfara mai shari’a Kulu Aliyu ta samu Kamal Yusuf da aikata laifukan ta kuma yanke mashi hukuncin kisa ta hanyar rataya, a yayin da kuma ta wanke Armayau Shehu daga dukkan zargi ta kuma sallame shi.

Idan dai za a iya tunawa a shekarar dubu 2013 aka kama Kamal Yusuf da abokansa su biyu bisa zargin kisan mahaifiyarsa Hajiya Hafsatu da kuma kannensa mata guda biyu wato Maryam da Amina.

Kamal ya yi fushi da mahaifiyar tashi bayan da taki yarda ta bashi dukiyar da kannensa suka gada daga mahaifinsu, wanda ta aura bayan rabuwarta da mahaifin Kamal.

Kamal ya gayyato abokansa suka kuma kashe mahaifiyar tashi da kannensa, suka jefa gawarwakinsu a cikin babban Dam na Gusau.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN