Type Here to Get Search Results !

Main event

Yadda jihohin arewa ke shirin yin taron dangi kan matsalar yan bindiga

Jihohin Arewacin Najeriya sun amince su yi aki tare domin yakar ‘yan bindiga da sauran matsalolin tsaro a yankin.

Gwamnonin jihohin Arewa maso yamma da takwaransu na jihar Neja sun amince su yi taron dangi wajen magance musamman matsalar ‘yan fashin daji.

Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya bayyana haka bayan ganawarsa da Shugaba Muhammadu Buhari kan matsalar tsaron da ke addabar jiharsa.

Tambuwal ya ziyarci shugaban ne domin neman karin dauki sakamakon harin ‘yan bindiga da suka hallaka mutum 60 a Karamar Hukumar Sabon Birni.

Gwamnan ya nemi a tura karin jami’an tsaro domin magance matsalar maharan da ke zubar da jinin jama’arsa.

Ya kuma nemi daukin Gwamantin Tarayya ga ‘yan jihar da ke gudun hijira sakamakon hare-haren ‘yan bindiga.

“Bayan hare-haren baya, kwana biyu da suka wuce ‘yan fashin daji sun hallaka mana kusan mutum 74 a harin da suka kai.

“Na yi wa shugaban kasa cikakken bayani tare da gabatar masa irin taimakon da mu da jami’an tsaro ke nema domin tababtar da tsaro,” a cewarsa.

A ranar Alhamis ne Shugaba Buhari ya umarci sojoji da su murkushe ‘yan ta’addan da ke addabar jihar Sokoto.

Rahotun Aminiya


DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies