Type Here to Get Search Results !

Soji da dansanda sun harbi juna da bindiga bisa tunanin yan ta'adda ne

Sojin kasar Kenya guda biyu tare da wani jami'in dansandan kasar, sun yi wa junansu mumunan raunuka bayan sun buda wa juna wuta da bindigogi bisa tunanin cewa yan ta'adda ne a Bura da ke yankin Garissa.

Rahotanni sun ce Kurtun dansanda Emmanuel Ngao ya harbi jami'an soji guda biyu David Mbugua da Jeremy Malusi bayan an sami zafafan cacan baki lokacin da suke zagayawan sintiri, sai suma suka mayar da martani suka harbe shi.

Shugaban yansandan Fafi George Singalao ya tabbatar da faruwar lamarin ya kuma ce an kai jami'an soji da na yansandan Asibitin Bura cikin mawuyacin yanayi sakamakon raunukan harbin bindiga.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN