Duba yadda aka kwashe Almajirai a Nassarawa zuwa jihohinsu

Rahotun BBC Hausa
Gwamnatin Nasarawa da ke tsakiyar Najeriya ta fara mayar da almajirai zuwa jihohinsu na asali.
Gwamnatin ta wallafa a Twitter hotunan almajiran yayin da suke shiga motocin da za su mayar da su jihohinsu.
Amma a sanarwar, gwamnatin Nasarawa ba ta bayyana jihohin da almajiran suka fito da za a mayar da su ba.
Rahotanni sun ce almajiran sun kai kusan 800 da gwamnatin ta tara za ta mayar da su garuruwansu. Kuma jihohin da rahotanni suka ce za a mayar da almajiran sun hada da Kaduna da Jigawa da Gombe da Filato da kuma jihar Taraba.
A karshen watan Afrilu ne Gwamnonin jihohin arewacin Najeriya 19 suka sanar da rufe dukkanin makarantun tsangaya da zummar shawo kan annobar korona a yankin.
Gwamnatin Kaduna ta ce almajiran da aka dawo da su daga Kano ne ya kara yawan adadin masu cutar korona a jihar.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN