Type Here to Get Search Results !

Duba yadda aka kwashe Almajirai a Nassarawa zuwa jihohinsu

Rahotun BBC Hausa
Gwamnatin Nasarawa da ke tsakiyar Najeriya ta fara mayar da almajirai zuwa jihohinsu na asali.
Gwamnatin ta wallafa a Twitter hotunan almajiran yayin da suke shiga motocin da za su mayar da su jihohinsu.
Amma a sanarwar, gwamnatin Nasarawa ba ta bayyana jihohin da almajiran suka fito da za a mayar da su ba.
Rahotanni sun ce almajiran sun kai kusan 800 da gwamnatin ta tara za ta mayar da su garuruwansu. Kuma jihohin da rahotanni suka ce za a mayar da almajiran sun hada da Kaduna da Jigawa da Gombe da Filato da kuma jihar Taraba.
A karshen watan Afrilu ne Gwamnonin jihohin arewacin Najeriya 19 suka sanar da rufe dukkanin makarantun tsangaya da zummar shawo kan annobar korona a yankin.
Gwamnatin Kaduna ta ce almajiran da aka dawo da su daga Kano ne ya kara yawan adadin masu cutar korona a jihar.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN