Type Here to Get Search Results !

Ba zamu lamunta da kashe mutane da sunan ramuwar gayya ba - Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya yi tur da matakin kashe kashen bayin Allah da sunan ramuwar gayya sakamakon tashin hankali tsakanin Fulani da Addara a jihar Kaduna.

Buhari ya ce ba daidai bane Fulani da Addarawa su dinga kashe junansu ta hanyar kai hari da ramuwar gayya ga junansu a karamar hukumar Kajuru na jihar Kaduna.

Ya ce daukan matakin taimaka wa kai marmakin amfani da doka shi ne dalili da ya ke jawo fadadar kashe kashen.

Bayanin haka ya fito ne daga bakin mai ba Buhari shawara kan harkar Labarai Garba Shehu, wanda ya ce shugaba Buhari ya yi gargadin cewa ba wanda ke da hurumin daukan doka a hannunsa.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN