Ba zamu lamunta da kashe mutane da sunan ramuwar gayya ba - Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya yi tur da matakin kashe kashen bayin Allah da sunan ramuwar gayya sakamakon tashin hankali tsakanin Fulani da Addara a jihar Kaduna.

Buhari ya ce ba daidai bane Fulani da Addarawa su dinga kashe junansu ta hanyar kai hari da ramuwar gayya ga junansu a karamar hukumar Kajuru na jihar Kaduna.

Ya ce daukan matakin taimaka wa kai marmakin amfani da doka shi ne dalili da ya ke jawo fadadar kashe kashen.

Bayanin haka ya fito ne daga bakin mai ba Buhari shawara kan harkar Labarai Garba Shehu, wanda ya ce shugaba Buhari ya yi gargadin cewa ba wanda ke da hurumin daukan doka a hannunsa.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN