An mayar da tarin Almajirai da yawa zuwa jihar Sokoto inda suka fito bayan sun shiga jihar Ondo ranar 4 ga watan Mayu.
Rahotanni sun ce Almajirai 25 sun sauka a motar tilera da ta dauko su, sai suka bi ta hanyar daji domin kauce wa jami'an tsaro, daga bisani suka sake ci wa motar suka hau a kan babban hanyar mota.
Kakakin hukumar yansandan jihar Ondo Tee Leo-Ikoro ya ce yansanda sun fitar da Almajiran daga jihar Ondo bayan hukumomi sun sanar da su. Ya ce an sami sa'ar kama Almajiran ne tsakanin kan iyakan jihar Kogi da kuma jihar Ondo.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari