Type Here to Get Search Results !

Yadda wasu magidanta makiyaya biyu suka kashe kansu wajen fada domin wata mata

Wasu makiyayan dabbobi guda biyu sun mutu bayan sun yi wa kansu munanan rauni da adda yayin da suke fada saboda wata mata a Oljorai da ke Gilgil a kasar Kenya.
 
Wannan lamari ya ba jama'a mamako ganin yadda aka sare wuyar daya daga cikin makiyayan kuma ya mutu nan take, yayin da dayan kuma ya mutu jim kadan bayan an kai shi wani Asibiti.
 
Wani ganau mai suna Abel Kiprokon ya ce, mutanen biyu suna soyayya da matar ce uwar yara uku, tun shekara biyu da suka gabata ba tare da sun sani ba sai daga bayannan
 
Mutanen guda biyu basu san junansu ba, sai ranar Laraba lokacin da daya daga cikinsu ya ga dayan yana karyawa da safe a gidan matar.

Daga bisani rigima ya sa mutanen biyu suka afka wa junansu ta hanyar yin amfani da adda.

Kwamishinan yankin Gilgil, Ndambuki Mutheki ya ce yansanda na gudanar da bincike kan lamarin, kuma sun kama matar da aka yi rikici a kanta.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya  

Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika 

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN