Wani Likita ya mutu sakamakon cutar coronavirus a jihar Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta sanar da mutuwar mutum daya sakamakon cutar coronavirus a jihar.
 
Gwamnan jihar Katsina Alhaji Aminu Masarin ne ya sanar da manema labarai haka. Ya ce wani Likita wanda ke zaune a garin Daura mai zaman kansa mai suna Dr. Aminu Yakubu, ya dawo daga Lagos sai ya rasu bayan kwanaki uku da dawowarsa.

Ya ce an kai samfur na jininsa NCDC  a birnin Abuja domin gwaji, daga bisani sakamakon gwaji da aka yi masa ya nuna yana dauke da cutar coronavirus.

Gwamna Masari ya ci gaba da cewa Dr Yakubu dan asalin jihar Kogi ne, kuma yana fama da cutar hawan jini da ciwon suga kafin ya kamu da cutar coronavirus wanda ake kyautata zaton cewa ya kamu da cutar ne lokacin da ya je Lagos
 
DAGA ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN