Type Here to Get Search Results !

Wani Likita ya mutu sakamakon cutar coronavirus a jihar Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta sanar da mutuwar mutum daya sakamakon cutar coronavirus a jihar.
 
Gwamnan jihar Katsina Alhaji Aminu Masarin ne ya sanar da manema labarai haka. Ya ce wani Likita wanda ke zaune a garin Daura mai zaman kansa mai suna Dr. Aminu Yakubu, ya dawo daga Lagos sai ya rasu bayan kwanaki uku da dawowarsa.

Ya ce an kai samfur na jininsa NCDC  a birnin Abuja domin gwaji, daga bisani sakamakon gwaji da aka yi masa ya nuna yana dauke da cutar coronavirus.

Gwamna Masari ya ci gaba da cewa Dr Yakubu dan asalin jihar Kogi ne, kuma yana fama da cutar hawan jini da ciwon suga kafin ya kamu da cutar coronavirus wanda ake kyautata zaton cewa ya kamu da cutar ne lokacin da ya je Lagos
 
DAGA ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN