Wata mata wacce ke dauke da cuytar coronavirus ta tsere daga wajen da akakillace masu cutar domin yi masu magani a kasar Ghana.
Jaridar Ghana City News, ta labarata cewa wanda ya tsere, yana daya daga cikin mutum takwas 'yan kasar Guinea da aka yi wa gwaji kuma suna dauke da cutar.
Wani babban Minista Salifu Saeed, ya ce wanda ta tsere mace ce wacce ke tsakanin shekarun 20 a rayuwa, ta ketare katangan ginin ne kuma ta bar kayakinta a wajen da aka killacesu a garin Tamale ranar Litinin.
Ya ce wannan abin tsoro ne domin matar tana dauke da cutar coronavirus tabbatacce, bayan gwajin da aka yi mata kafin killace ta kuma sai ga shi ta tsere ta shiga cikin jama'a.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya
Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari