Gobara ta hallaka mutane ta kone sama da gidaje 50 a Legas

Rahotun Jaridar Aminiya


Da safiyar ranar Lahadi ne al’ummar unguwar Abule Ado da ke yankin Festak a karamar hukumar Amuwo Odofin a jihar Legas, suka wayi gari da karar fashewar wasu abubuwa wadanda suka yi sanadiyyar tashin gobarar da tayi salwantar rayuka da dama da kuma kone tare da lalata akalla gidaje 50 a yankin.

Wasu mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa, gobarar ta samo asali ne bayan da wata motar tifa da ke sauke kasa a yankin ta kama da wuta, inda nan take wutar ta yadu zuwa sassan da bututun man fetur ke shinfide a karkashin kasa.

Kana zuwa yanzu jami’an kashe gobara ta gwamnatin jihar Legas da na tarayya sun yi kokarin kashe wutar, haka zalika jami’an hukumar bada agajin gaggawa ta kasa wato NEMA a takaice sun isa wajen domin bada agaji.

Babban jami’in hukumar da ke kula da shiyyar jihohin Kudu maso Yamma Ibrahim Farinloye, ya shaida cewa wutar ta tashi ne daga inda bututun man fetur din suke, ya ce an girke manyan motocin kashe gobara 3 da suke aikin kashe wutar kana zuwa yanzu ba za a iya sanin adadin mutanen da suka hallaka sakamakon gobarar ba, sai dai gidaje akalla 50 sun salwanta a sakamakon ibtila’in.

DAGA ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya  

Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika 

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN