Type Here to Get Search Results !

Gobara ta hallaka mutane ta kone sama da gidaje 50 a Legas

Rahotun Jaridar Aminiya


Da safiyar ranar Lahadi ne al’ummar unguwar Abule Ado da ke yankin Festak a karamar hukumar Amuwo Odofin a jihar Legas, suka wayi gari da karar fashewar wasu abubuwa wadanda suka yi sanadiyyar tashin gobarar da tayi salwantar rayuka da dama da kuma kone tare da lalata akalla gidaje 50 a yankin.

Wasu mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa, gobarar ta samo asali ne bayan da wata motar tifa da ke sauke kasa a yankin ta kama da wuta, inda nan take wutar ta yadu zuwa sassan da bututun man fetur ke shinfide a karkashin kasa.

Kana zuwa yanzu jami’an kashe gobara ta gwamnatin jihar Legas da na tarayya sun yi kokarin kashe wutar, haka zalika jami’an hukumar bada agajin gaggawa ta kasa wato NEMA a takaice sun isa wajen domin bada agaji.

Babban jami’in hukumar da ke kula da shiyyar jihohin Kudu maso Yamma Ibrahim Farinloye, ya shaida cewa wutar ta tashi ne daga inda bututun man fetur din suke, ya ce an girke manyan motocin kashe gobara 3 da suke aikin kashe wutar kana zuwa yanzu ba za a iya sanin adadin mutanen da suka hallaka sakamakon gobarar ba, sai dai gidaje akalla 50 sun salwanta a sakamakon ibtila’in.

DAGA ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Latsa nan ka zabi masoyiyarka daga jerin 'yan mata da ke neman aure ko soyayya  

Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika 

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN