Type Here to Get Search Results !

An sa dokar ta baci a Kaduna, kowa ya zauna a gida

Rahotun Legit Hausa

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar ta baci a fadin jihar saboda mutane sun sabawa dokokin farko da gwamnatin ta sanya domin hana shigowa da yaduwar cutar Coronavirus jihar. Mataimakiyar gwamnan, Hadiza Balarabe, wacce ta sanar da hakan ranar Alhamis ta ce wannan shawara da aka yanke ya yi muwafaqa da kudin tsarin mulkin Najeriya.

A cewarta, kwamiti na musamman kan yakar cutar ta gana domin tattauna yadda cutar ke cin rayuka sauran jihohi da kasashen waje. Tace: "Kwamitin ta samu rahoton cewa mutane sun sabawa dokokin hana taro a sanarwa daban-daban da tayi cikin kwanaki bakwai da suka wuce."

 "An samu rahotonnin mutane sun yi ko oho da dokar hana hawa babur, Keken 'a daidaita sahu' , da motoci fiye da fasinjoji biyu a kujera da aka sanya." "Saboda haka, daga daren Alhamis, 26 ga Maris 2020, wajibi ne dukkan mazauna jihar Kaduna su zauna a gida . Babu zuwa aiki, babu kasuwanci, babu zuwa wuraren ibada."

"Mutanen da aka amincewa fitowa kadai sune jami'an kwana-kwana, jami'an kiwon lafiya da jami'an tsaro." "Za'a kulle Masallatai da cocuna, babu Sallar Jami'in da za'a amince a gudanar ciki ko waje." "Duk wajen Ibada ko taron da aka kama ana taro, lallai sun saba doka kuma za'a iya kwace takardan mallakan filin wajen ko kuma kwace wajen."

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN