Type Here to Get Search Results !

Yanzu yanzu: Saurayi dan shekara 23 ya kashe Mahaifi da Mahaifiyarsa, karanta dalili

Da sanyin safiyar Talata, wani saurayi mai suna Michael Okibe, mai shekara 23, ya kashe mahaifinsa wanda Lauya ne mai suna Barista Clement Okibe, ya kuma kashe mahaifiyarsa mai suna Toyin, bayan ya caka masu wuka, kuma jini ya yi ta zuba har suka mutu.

PM Express ta ruwaito cewa lamarin ya faru a unguwar Alhaji Afeez Gbadomosi da ke yankin Ejigbo a birnin Ikko,watau Lagos.

Hakazalika, rahotun ya ce Maichael bai bar yar'uwarshi mai suna Mary ba, domin ita ma ya caka mata wuka, kuma yanzu haka tana wani Asibiti inda take jinya rai hannun Allah.

Makwabta sun ce uwayen Michael sun sha wuya a kansa, domin dai sun sha kai shi Jami'a na kudi masu zaman kansu domin ya yi karatu, amma karshen lamari shi ne ana koroshi daga Jami'an saboda rashin kokari, sakamakon harka da kwayoyi da kayan maye.

Gidan Barista Clement inda Michael ya kashe uwayensa
Yansandan sashen Ejigbo sun dauki gawakin iyayen Michael, suka kai su babban Asibitin gwamnatii na Isolo, domin  gudanar da bincike kan musabbabin mutuwarsu.

Bayanai sun ce Michael, sanye da gajeren wandon Boxer, ya gidu daga gida, bayan ya kashe iyayensa tare da raunata yar uwarshi da wuka. Sai dai tuni yansanda suka shiga farautar Michael.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN