Type Here to Get Search Results !

Main event

Rashin sauke manyan jami'an tsaro: Za mu kai Buhari kara a Kotu - Inji Falana

Fitaccen Lauya Femi Falana, ya bayyana aniyarsa ta gurfanar da shugaba Muhamadu Buhari a gaban Kotu, sakamakon rashin sallamar manyan jami'an tsaron Najeriya duk da kiraye kiraye da jama'a ke yi a kan lamarin.

Falana ya furta wadannan kalamai ne lokacin da yake tattaunawa da gidan Talabijin na Channels, ya ce "Shugabannin tsaron sun zarce shekara 35 na aiki kamar yadda doka ta shata".

A tattaunawar, Falana ya kara da cewa " Karkashin dokokin aikin Najeriya, kuma karkashin dokokin aikin sojin Najeriya, sashe na 6 na dokokin aikin soji, an ba shugaban kasa dama ya yi dokoki, amma ba inda dokar ta ba shi dama ya tsawaita wa'adin aikin shugabannin tsaro fiye da lokaci da doka ta kayyade".

" Can baya an yi haka, amma wannan ba hujja bane. Dole kowa ya kasance daidai da kowa a fuskar doka, ba adalci bane ka ce ma wasu su ajiye aiki domin sun cika shekara 35 suna aiki, lokaci daya kuma ka kara wa'adin aiki ga wasu, bayan sun zarce shekara 35 suna aiki, ko sun cika wa'adin shekara 60 da haihuwa".



" Na san za a shigar da kara a kan wannan lamari" inji Falana.


DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies