Ma'aikaciyar jinyar da take rawa don karfafa gwiwar marasa lafiya

Rahotun BBC Hausa

Wata ma'aikaciyar jinya a Afirka ta Kudu na rawa saboda ta sanya marasa lafiya nishadi.

Jaridar Daily Sun ta kasar, ta nuna hoton bidiyon ma'aikaciyar, Thathakahle Gumede, 'yar shekara 57 tana ta taka rawa a gaban marasa lafiyan da suke jira su ga likita a wani asibiti da ke KwaZulu-Natal.
Ms Gumede ta ce tana taka rawar ne domin marasa lafiyar da ke wajen su samu kwarin gwiwa a kan cutar da ke damunsu.

Ta ce "Na yi amanna cewa magani ne ke warkar da ciwo, amma kuma mu ma ma'aikatan jinya na da rawar ta kawa wajen warkewar marar lafiya".

Ms Gumede ta ci gaba da cewa "Yana da matukar muhimmanci ma'aikatan jinya su rinka yin abubuwan da za su sanyaya zukatan marasa lafiya, ba abin da zai bata musu ba".

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN