Rahotun Legit Hausa
Tsohon shugaban Najeriya, Ibrahim Badamasi Babangida, ya yi
hira da Jaridar Daily Trust a karshen makon nan, inda ya tabo batutuwa wanda su
ka shafi harkar tsaro. A na sa shawarar, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, ya
bayyana cewa ya kamata gwamnati ta dage wajen samun bayanan sirri game da yadda
‘yan Boko Haram su ke aiki.
Haka zalika tsohon Sojan Najeriyar ya nuna cewa akwai bukatar Sojojin Najeriya su san wanene manyan shugabannnin Boko Haram da kuma inda su ke samun horaswa. Ibrahim Babangida ya bayyana cewa Mayakan Boko Haram tsirarrun ‘Yan ta’adda ne kuma ba Sojojin yaki ba ne don haka su ke kokarin jefa tsoro a cikin zukatan ‘Yan kasa.
Bayan haka, tsohon shugaban kasar ya ce akwai bukatar a rika
fadakar da jama’a tare da jan hankalinsu game ta’adin ‘Yan kungiyar, IBB ya ce
wannan yaki na kowa ne. IBB wanda ya mulki Najeriya daga 1985 zuwa 1992 ya
bayyana cewa dole sai kowa(Soja da farar hula) ya taka irin na sa rawar ganin
wajen kawo karshen rigimar Boko Haram.
Janar Babangida ya bayyana cewa an dade ana samun rigingimu
a Najeriya tun farkon kafuwar kasar. Sai dai tashin hankali ya yi kamari ne
daga bayan zuwa Soji zuwa yanzu. A cewar Babangida, bayan yakin basasa a farkon
shekarun 1970s, an yi ta fama da matsalar fashi da makami, amma da gwamnati ta tsaya
tsayin-daka, sai da aka magance matsalar.
A hirar da ya yi da Daily Trust, tsohon shugaban kasar ya
koka da yadda Dajin Sambisar da aka rika horas da Sojojin Najeriya a baya, ya
koma hannun ‘Yan ta’addan Boko Haram. A game da Dakarun Amotekun, Babangida ya
nuna cewa akwai alamun cewa aiki ya yi wa Sojoji yawa. IBB kuma ya ce a
lokacinsa, Hafsun Sojoji su na da wa'adin shekaru hudu ne,
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari