Yanzu-yanzu- An yi garkuwa da sakataren gwamnati a wata jihar arewa


Rahotun Legit Hausa

Wasu yan bindiga sun yi garkuwa da sakataren din-din-din na ma’aikatar ayyukan a jahar Nasarawa, Alhaji Jibrin Giza, a tsakar daren ranar Asabar. Kwamishinan yan sanda a jahar, Mista Bola Longe, ya tabbatar da lamarin ga kamfanin dillancin labaran Najeriya a Lafia.

Longe ya fada ma NAN cewa yan bindiga sun sace sakataren din-din-din din daga gidansa a Shabu, wani yanki na Lafia da misalin 12:40 na tsakar dare zuwa wani wuri da ba a sani ba. A cewar kwamishinan yan sandan, Shugaban yan sanda a yankin ya rigada ya zuba wasu jami’ai wadanda za su bi sahun masu garkuwan da suka tsere da wadanda suka sace.

Longe ya kara da cewa ya umurci mataimakin kwamishina na ayyuka, jami’in da ke kula da rundunar yaki da fashi na musamman, da su kakkabe yankin don tabbatar da sun ceto wadanda aka sace da kuma kama masu garkuwan. Ya kuma sha alwashin cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai ta ceto wadanda aka sace. Longe ya kara da cewa masu garkuwan ba su kira yan’uwan wadanda suka sace ba tukuna. 


DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN