Type Here to Get Search Results !

Yanzu-yanzu- An yi garkuwa da sakataren gwamnati a wata jihar arewa


Rahotun Legit Hausa

Wasu yan bindiga sun yi garkuwa da sakataren din-din-din na ma’aikatar ayyukan a jahar Nasarawa, Alhaji Jibrin Giza, a tsakar daren ranar Asabar. Kwamishinan yan sanda a jahar, Mista Bola Longe, ya tabbatar da lamarin ga kamfanin dillancin labaran Najeriya a Lafia.

Longe ya fada ma NAN cewa yan bindiga sun sace sakataren din-din-din din daga gidansa a Shabu, wani yanki na Lafia da misalin 12:40 na tsakar dare zuwa wani wuri da ba a sani ba. A cewar kwamishinan yan sandan, Shugaban yan sanda a yankin ya rigada ya zuba wasu jami’ai wadanda za su bi sahun masu garkuwan da suka tsere da wadanda suka sace.

Longe ya kara da cewa ya umurci mataimakin kwamishina na ayyuka, jami’in da ke kula da rundunar yaki da fashi na musamman, da su kakkabe yankin don tabbatar da sun ceto wadanda aka sace da kuma kama masu garkuwan. Ya kuma sha alwashin cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai ta ceto wadanda aka sace. Longe ya kara da cewa masu garkuwan ba su kira yan’uwan wadanda suka sace ba tukuna. 


DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN