ISYAKU.COM ya samo cewa hadimin Gwamnan, ya yi karar ne ranar 7 ga watan Janairu kwana daya kafin wasu Mawakan su gurfana a gaban Kotun Majistare, sakamakon kara da Gwamnan jihar Kebbi ya shigar a gaban Kotu, wanda ke dauke da koken kara kwatankwacin irin wanda Dr Haliru ya shigar a kan Mawakan.
Tuni Mawakan suka yi hayan Lauyoyi domin kare su a gaban Kotu bisa tuhuma da suke fuskanta kan zargin cin zarafi da mutuncin Gwamnan Kebbi da hadimansa a cikin wakar da suka rera.
Sai dai kawo yanzu, Kotu bata sa ranar sauraron kara da Dr. Haliru ya shigar ba a gabanta kawo yanzu da muka wallafa wannan rahotu.
Sai dai za a ci gaba da shari'ar da Gwamnan jihar Kebbi ya shigar kan Mawakan ranar 9 ga watan Janairu a babban Kotu Majistare da ke garin Birnin kebbi.
DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA Facebook.com/isyakulabari Twitter.com/isyakulabari