Wasu kungiyoyi masu karadin ganin an sami zaman lafiya tare da bin doka da oda tsakanin al'umma sun yi tur tare da Allah wadai bisa yadda wasu Mawaka a jihar Kebbi da arewacin Najeriya suka rera wakar batanci ga wani shugaba kuma babban dan siyasa a jihar.
Kungiyoyin, karkashin jagforancin Abubakar Muhammed ABK, sun fitar da wannan sanarwa ne jim kadan bayan wani taro da suka gudanar a garin Birnin kebbi, inda suka tattauna kan yadda za a tafiyar da sulhu tsakanin mai kara da wadanda aka yi kara a Kotu, tare da kauce wa sake faruwan irin haka nan gaba, bayan sun nuna rashin jin dadi tare da rashin amfanin aukuwan irin wannan lamari a cikin al'umma.
Kungiyoyi da shugabanninsu suka wakilce su a wajen wanann taro sun hada da:
1. Abubakar Abk -Film writers Association
2. Atiku ciroma- state chairman Sakai
3. S Kudu Chairman- chairman matasa kan harkokin democradiya
4. Ibrahim Sani Master
5. Nafiu Zaki - Chairman kabukabu
6. Faruku Gaga- chairman KeKe napep
7. Mustapha Aliyu Gwadangaji - Chairman Youth development Gwadangaji
7. Mustapha Aliyu Gwadangaji - Chairman Youth development Gwadangaji
8. Abubakar Sadiq - Chairman Social Media
9. Jabir Jega - Matasan mawaka
10. Abubakar Udu - Chairman KATA kebbi state
13. Chairman Youth soccer Kebbi state
DAGA ISYAKU.COMLatsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari