Yansanda sun aika wasu mutum biyu lahira da gaggawa, duba dalili

Jami'an  rundunar yansandan jihar Anambra sun yi nassarar bindige yan fashi da makami guda biyu bayan wani musanyar wuta da bindigogi. Wadanda aka kashe su ne Onyebuchi Ngala wanda aka fi sani da suna Ceaser da kuma Izuchukwu Okoro.

Kakakin hukumar yansanda na jihar Muhammed Haruna, ya ce wadanda aka kashe, sun dade suna addabar mazauna  birnin Awka da kewaye. Ya ce yansanda sun bi su zuwa maboyarsu a Nkwo Agulu, kuma ganin yansanda ke da wuya sai yan fashin suka buda ma yansanda wuta ta hanyar harbi da bindigogi.

Sakamakon haka yansanda suka mayar da martani kuma suka aika yan fashin barzahu.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN