SADA ILU tsohon Daraktan DSS ya rasu

Allah ya yi wa Alhaji Sada Ilu rasuwa a birnin Cairo na kasar Egypt watau Misira . Jigo a jam'iyar APC a jihar Katsina kuma tsohon Darakta a hukumar tsaro na farin kaya DSS.

Gwamnan jihar Katsina Aminu Masari ya bayyana marigayi Sada cewa rayuwarsa abin koyi ne ga al'umman jihar Katsina a wata sanarwa da ta fito daga hannun Darakatan watsa labarai na gidan Gwamnati Abdu Labaran ranar Lahadi.

Sada ya rike mukamai da dama a lokacin aikinsa a DSS, kuma daya daga cikin wadanda yan arewacin Najeriya a hukumar suka amfana matuka da shi sakamakon yadda ya ke yin tsaye ka'in da na'in domin ganin ba a zalunci yan arewa ba a hukumar.

Duniyar tsofaffin ma'aikatan hukumar DSS masu murabus za su tuna da karamci, mutunci, taimako da martaban Sada Ilu har iya rayuwarsu.

DAGA ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp

https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN