Yar Najeriya Maryam Sanda, ta kasa rike hawayenta da suka yi da zubowa sakamakon kuka da ta dinga yi ba kakkautawa bayan Alkalin babban Kotu a birnin tarayyar Najeriya Abuja ya yanke mata hukuncin kisa ta hanyar ratayeta har ta mutu.
Alkalin Kotun Jastis Yusuf Halilu ya same ta da laifin kashe mijinta Bilyaminu Bello.
Yanke hukuncin ke da wuya, Maryam Sanda ta fashe da kuka, kuma ta kasa iya rike kanta, amma a bayyane yake cewa Lauyanta, tare da jami'an Kurkuku, sun yi ta lallashinta kafin daga bisani aka fita da Maryam da gudu daga cikin Kotu, yayin da Manema labarai suka bita da gudu suna daukan hotuna da bidiyo kafin a sakata a cikin mota.
Alkalin Kotun ya ce tana da dama ta daukaka kara.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari